Bayan da sojojin suka yi ma Yesu ba’a, sai suka kai shi wani wuri suka giciye shi. Suka sa ya ɗauki giciyen bisan wanda zai mutu.
Sojojin suka kai Yesu wani wuri da ake kira Golgota, kuma suka kafa masa ƙusoshi a hannuwa da ƙafafuwa a jikin giciyen. Amma Yesu ya ce, “Uba, ka gafarta masu, gama ba su san abin da suke yi ba.” Bilatus ya umurce su, su rubuta,“Sarkin Yahudawa” bisan wata alama, kuma su ɗaura shi kan giciye sama da kan Yesu.
Sojojin suka jefa kuri’a a kan kayan Yesu. Da suka yi haka nan, sun cika annabci da ya ce, “Sun raba kayana a tsakaninsu, kuma sun jefa kuri’a a kan tufafina.”
Yesu an giciye shi a tsakanin ɓarayi biyu. Ɗaya daga cikinsu ya yi wa Yesu ba’a, amma ɗayan ya ce, “Ba ka da tsoron Allah? Mun yi laifi, amma wannan mutumen maras laifi ne.” Sai ya cewa Yesu,“In ka yarda ka tuna da ni a cikin mulkinka.” Yesu ya amsa masa cewa, “Yau, za ka zauna tare da ni a cikin Aljanna.”
Shugabannin Yahudawa da sauran mutane cikin taron suka yi wa Yesu ba’a. Suka ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, sauko daga giciyen, kuma ka ceci kanka! Sa’anan sai mu bada gaskiya gareka.”
Da samaniya bisan dukan wurin ta yi baƙi gaba ɗaya, ko da yake cikin tsakiyar rana ne, sai duhu ya tsaya har zuwa ƙarfe uku na maraice cikin duka ƙasa.
Sai Yesu ya ɗaga murya, “An ƙare! Uba, ina sakin ruhuna a hannuwanka.” Sai ya sadda kai, kuma ya bar ruhunsa. Da ya mutu, sai aka yi girgizar ƙasa, kuma sai labulen da yake raba mutane daga hallarar Allah ya rabu a biyu daga sama zuwa ƙasa.
Ta wurin mutuwarsa, Yesu ya buɗe wa mutane hanyar zuwa wurin Allah. Da sojin da yake gadi ya ga duk abin da ya faru, ya ce, “Na tabbata wannan mutum maras laifi ne. Shi Ɗan Allah ne.”
Sai Yusufu da Nicodemus, shugabannin Yahudawa biyu da suka gaskanta da Yesu Almasihu ne, suka tambayi Bilatus jikin Yesu. Suka nanaɗe jikin cikin zane, kuma suka sa shi cikin kushewa da aka gina cikin dutse. Sai suka gangaro da babban dutse a gaban kushewar suka rufe ƙofar.