Open Bible Stories Home

20. Gudun Hijira da Komawa

Labarin LMT daga : 2 Sarakuna 17; 24-25; 2 Labarbaru 36; Ezra 1-10; Nehemiya 1-13

Mulkin Isra’ila da mulkin Yahuda duka sun yi wa Allah zunubi. Sun karya alkawalin da Allah ya yi masu a Sinai. Allah ya aike da annabawansa su fadakar da su, su tuba, kuma su bauta mashi, amma sun ƙi su yi biyayya.

Sai Allah ya hori dukan mulkokin ta barin abokan gaba su hallaka su. Daular Asuriya, al’umma mai ƙarfi, da ƙeta, suka hallaka mulkin Isra’ila. Asuriyawan suka kashe mutane da yawa cikin mulkin Isra’ila, suka ɗauke dukan abubuwa masu tamani, suka ƙone yawancin ƙasar.

Asuriyawa suka tattara dukan shugabanni, masu arziki, masu amfani, kuma suka tafi da su Asiriya. Matalauta Isra’ilawa, wanda ba a kashe ba kaɗai, suka yi saura a Isra’ila.

Sai Asuriyawa suka kawo baƙi su zauna cikin ƙasar Isra’ila ta da. Baƙin suka sake gina garuruwan da aka hallaka, kuma suka auri Isra’ilawan da suka yi saura. Zuriyar Isra’ilawan da suka auri baƙi sunanansu Samariyawa.

Mutanen cikin mulkin Yahuda suka ga yadda Allah ya hori mutanen mulkin Isra’ila domin rashin bada gaskiya da rashin biyayya gareshi. Amma duk da wannan sun ci gaba da bautar gumaka, har da allolin Can’aniyawa. Allah ya aike da annabawa su faɗakar da su, amma sun ƙi su ji.

Wajen shekara 100 bayan da Asuriyawa suka hallaka mulkin Isra’ila, Allah ya aika Nebukadnezzar, sarkin Babila, ya faɗa mulkin Yahuda da yaƙi. Babila babbar daula ce, mai ƙarfi kuma. Sarkin Yahuda ya yarda ya zama bawan Nebukadnezzar, kuma ya biya haraji mai tsada kowace shekara.

Amma bayan ƴan shekaru kaɗan, Sarkin Yahuda ya tayaswa Babila. Sai mutanen Babila suka koma, suka faɗa mulkin Yahuda. Suka ci garin Urshalima, suka hallaka Haikalin, kuma suka ɗauke dukan arzikin garin da Haikalin.

Domin horon sarkin Yahuda da yin tawaye, sojojin Nebudkanazzer suka kashen ƴaƴan sarkin a gaban idonsa, kuma suka makauta shi. Bayan wannan, sai suka kai sarkin kurkuku, ya mutu a Babila.

Nebukadnezzar da rundunar sojojinsa suka kai yawancin mutanen mulkin Yahuda zuwa Babila, sai suka bar matalauta a baya su shuka gonaki. Wannan lokacin da mutanen Allah aka fitar da su da ƙarfi daga ƙasar alkawali ana kiranshi Gudun Hijira.

Ko da yake Allah ya hori mutanensa don zunubinsu ta wurin kai su gudun hijira, bai manta da su ba, ko alkawalainsa. Allah ya ci gaba da lura da su, kuma da magana da su ta wurin annabawa. Ya yi alkawali da cewa bayan shekara saba’in, za su koma ƙasar alkawali.

Da shekara saba’in suka cika, Sirius, sarkin Fashiya ya ci Babila da yaƙi, sai Daular Fashiya suka yi kanbacin Daular Babila. Isra’ilawa yanzu ana kiransu Yahudawa, kuma yawancin su sun zauna a Babila. Yahudawa ƙalilan ne, kuma tsofofi ne ƙadai suke tune da ƙasar Yahuda.

Daular Fashiya tana ƙarfi amma kuma da juyayin mutanen da suka kamo. Lokaci kaɗan bayan da Sirius ya zama sarkin Fashiyawa, ya bada umurni cewa duk Bayahude da yake so ya koma Yahuda, yana iya barin Fashiya ya koma Yahuda. Ya kuma bada kuɗin sake gina Haikalin! Ke nan bayan shekara saba’in na gudun hijira, wasu Yahudawa suka koma garin Urshalima cikin Yahuda.

Da mutanen suka iso Urshalima, suka sake gina Haikalin da kuma garun garin. Duk da wannan waɗansu mutane ne suke mulkinsu. Hallo kuma suna zaune a ƙasar alkawali, kuma suna sujada a Haikalin.

Sura mai zuwa