Bayan mutuwar Yusufu, dukan ƴan’uwansa suka zauna a Masar. Su da zuriyarsu suka ci gaba da zama shekaru da yawa har suka haifi ƴaƴa da yawa. Ana kiransu Isra’ilawa.
Bayan shekaru ɗaruruwa, yawan Isra’ilawa ya ƙaru sosai. Masarawa sun manta da Yusufu da duk abin da ya yi na taimakonsu. Sun ji tsoron Isra’ilawa don sun riɓanɓanya. Sai Fir’auna da yake iko a wannan lokacin ya maida Isra’ilawan bayin masarawa.
Masarawan suka sa isra’ilawan su yi gini-gine har da ɗumbin garuruwa. Aikin mai wuya ya tsanantawa rayuwarsu, amma Allah ya albarkace su, sai suka ƙara haifuwar ƴaƴa.
Fir’auna ya ga Isra’ilawa suna ta samu haifuwa da yawa, sai ba mutanensa umarni su kashe dukan jarirai maza na Isra’ilawa, ta jefa su cikin kogin Nilu.
Wata macen Isra’ila ta haifi ɗa namiji. Ita da mijinta sun ɓoye yaron tsawon lokacin da suke iyawa.
Sa’ad da uwayen yaron ba su iya ɓoye shi, sai suka sa shi cikin kwando bisan ruwa cikin kyauro a bakin kogin Nilu don ta cece shi daga makasa. Ƴar’uwarsa tana lura ta gani abin da zai faru da shi.
Gimbiya ƴar Fir’auna ta ga kwandon, kuma ta duba ciki. Da ta gani jariri ne, ta ɗauke shi kamar ɗanta na cikinta. Ta ɗauki mace Bayahudiya ta yi renon shi, ba ta san da cewa ba macen ita ce uwar yaron ta gaskiya. Da yaron ya girma an yaye shi, ta maida wa ƴar Fir’auna, ita kwa ta kira sunansa Musa.
Wata rana lokacin da Musa ya yi girma. ya gani wani Bamasare yana bugon Bayahude bawa. Musa ya yi ƙoƙari ya ceci ɗanuwansa Bayahude.
Da Musa ya ga ba mai ganinshi, sai ya kashe Bamasaren, ya kuma binne jikinsa. Amma akwai wanda ya ga duk abin da Musa ya yi.
Da Fir’auna ya ji labarin abin da Musa ya yi, sai ya so ya kashe shi. Musa ya gudu daga Masar zuwa cikin jeji inda ya kuɓuta daga hannun sojojin Fir’auna.
Musa ya zama makiyayi cikin jeji nesa da Masar. Ya auri mata a wannan wuri, ya haifi ɗiya biyu.
Wata rana sa’ada Musa yake kiwon tumakinsa, ya ga kurmi yana cin wuta. Amma kurmin bai ƙone ba. Musa ya kusato da kurmin don ya gani da kyau. Da ya matso kusan kurmin mai cin wuta, sai muryar Allah ta ce, “Musa, fid da takalmanka. Wurin da kake mai tsarki ne.”
Allah ya ce, “Na ga wahalar mutanena. Zan aike ka wurin Fir’auna don ka fitar da Isra’ilawa daga bautarsu daga cikin Masar. Zan basu ƙasar Kan’ana, ƙasar da na wa Ibrahim, Ishaƙu, da Yakubu alkawali.”
Musa ya yi tambaya, “In mutane suka tambaya wa ya aiko ni, me zan ce?” Allah ya ce, “NI NE WANDA YAKE NI NE. Ka ce masu ‘Ni ne ya aiko ni wurinku’. Ka kuma gaya masu ‘Ni ne Yahweh, Allah kakanninku Ibrahim, Ishaƙu da Yakubu’. Wannan sunana ne har abada.’”
Musa ya tsorota kuma ba ya so ya je wajen Fir’auna ba don yana tunanin ba zai iya magana ba da kyau, sai Allah ya aiko da ɗanuwan Musa, Haruna, don ya taimake shi. Allah ya faɗakar da Musa da Haruna cewa da Fir’auna zai taurare zuciyarsa.