Bayan shekaru da dama, Dauda ya mutu, kuma ɗansa Sulemanu ya fara mulkin Isra’ila. Allah ya yi magana da Sulemanu, kuma ya tambaye shi me ya fi so. Da Sulemanu ya tambayi hikima, Allah ya yi daɗi, sai ya mayas da shi wanda ya fi hikima cikin dukan duniya. Sulemanu ya koyi abubuwa da yawa, kuma zama alkali mai hikima. Allah ya kuma bashi arziki da yawa.
A Urshalima, Sulemanu ya gina Haikalin da ubansa Dauda ya nufa ya yi har da ya tara kayan ginin. Mutane, yanzu suna bautar Allah, kuma suna miƙa hadayu gareshi a Haikalin maimakon cikin alfarwa ta taruwa. Allah ya sauko cikin Haikalin, ya zauna tare da mutanensa.
Amma Sulemanu ya ƙaunaci mata na wasu ƙasashe. Ya yi wa Allah rashin biyayya da ya auri mata da yawa, kusan 1,000. Yawancin matan sun fito daga baƙin ƙasashe, kuma sun zo da allolinsu tare da su, suka ci gaba da bauta masu. Da Sulemanu ya tsufa, shi ma ya bauta masu.
Allah ya yi fushi da Sulemanu, kuma domin horon rashin riƙe bangaskiyar shi, sai ya alkawarta ya raba al’umma Isra’ila cikin mulki biyu bayan mutuwar Sulemanu.
Bayan mutuwar Sulemanu, ɗansa Rehobowam ya zama sarki. Rehobowam ba mutum mai hankali ba ne. Dukan mutanen al’umma Isra’ila suka zo tare suka naɗa shi sarki. Suka kai ƙara cewa Sulemanu ya ɗaura masu aiki mai nauyi da haraji mai ɗumbun yawa.
Rehobowam ba tunani sai ya amsa masu, “Kuna tunani ubana Sulemanu ya sa ku aiki mai wuya, amma zan sa ki fi wannan aiki, kuma zan hore ku fiye da shi.”
Goma daga cikin kabilun al’ummar Isra’ila suka tayas wa Rehobowam. Kabila biyu kaɗai suka tsaya da shi. Waɗannan kabilun biyu suka zama mulkin Yahuda.
Sauran kabilu goma na al’ummar Isra’ila da suka tayas wa Rehobowam, suka ɗauki wani mutum mai suna Yerobowam ya zama sarkinsu. Sai suka kafa mulkinsu a arewacin ƙasar, kuma suka kira mulkinsu Isra’ila.
Yerobowam ya wa Allah tawaye, kuma ya sa mutane zunubi. Ya gina gumaka biyu domin mutanensa su bauta masu maimakon su bauta ma Allah a Haikalin mulkin Yahuda.
Mulkin Yahuda da na Isra’ila suka zama abokan gaba, kuma sukan ya yaƙi tsakaninsu.
Cikin sabon mulkin Isra’ila, duka sarakai mugaye ne. Da yawa daga cikinsu sun mutu a hannun sauran Isra’ilawan da suke neman sarauta a kabancinsu.
Dukan sarakuna da yawancin mutanen mulkin Isra’ila suna bautar gumaka. Bautar gumakan tana ƙumshe da mugunyar jima’i da kuma wata sa’a hadayar yara.
Sarakunan Yahuda zuriyar Dauda ce. Waɗansu daga cikinsu mutane masu kirki, su kuma yi mulki da adalci, sun bauta wa Allah. Amma yawancin sarakunan Yahuda mugaye ne, mazambata ne, kuma suna bautar gumaka. Daga cikinsu wasu har sun miƙa ɗiyansu hadaya ga alloli na banza. Yawancin mutanen Yahuda suma suka tayarwa Allah, kuma suka bauta wa waɗansu alloli.