Open Bible Stories Home

22. Haifuwar Yahaya

Labarin LMT daga Luka 1

A zamanin da Allah ya yi magana da mutanensa ta wurin mala’iku da annabawa. Amma shekaru 400 suka wuce bai yi magana ba. Ba zato ba tsammani wani mala’ika ya zo da saƙo daga Allah zuwa wani tsofon firist mai suna Zakariya. Zakariya da matarshi Alisabatu, mutanen Allah ne, amma ba ta samu sa’ar haifuwa ba tukuna.

Mala’ikan ya cewa Zakariya, “Matarka za ta haifi ɗa. Za ka raɗa masa sunan Yahaya. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki, kuma zai shirya mutanen domin Almasihu!” Zakariya ya amsa, “Matata da ni, mun tsufa da yawa domin haifuwar ƴaƴa! Ƙaƙa zan sani wannan zai faru?”

Mala’ikan ya amsawa Zakariya, “Allah ya aiko ni in kawo maku labari mai daɗi. Domin ba ka gaskanta ba, ba za ka yi magana ba har sai an haifi ɗan.” Nan da nan sai Zakariya ya bebance. Sai mala’kan ya bar Zakariya. Bayan haka, Zakariya ya koma gidansa, kuma mata tasa ta ɗauki ciki.

Lokacin da Alisabatu tana da cikin wata shida, wannan mala’ikan, ba zato ba tsammani ya sake bayyanuwa ga ƴar uwar Alisabatu mai suna Maryamu. Budurwa ce, kuma wani saurayi mai sunan Yusufu yana tashenta. Mala’ikan ya ce, “Za ki yi ciki, kuma za ki haifi ɗa. Za ki kira sunansa Yesu. Zai zama Ɗan Allah Maɗaukaki, kuma zai yi mulki har abada.”

Maryamu ta amsa ta ce, “Yaya wannan zai yi faru tunda yake ni budurwa ce?” Mala’ikan ya kwatamta mata cewa, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, kuma ikon Allah zai lulluɓe ki. Jaririn zai zama mai tsarki, Ɗan Allah.” Maryamu ta gaskanta, ta kuma yarda da abin da mala’ika ya faɗa.

Dan lokaci kaɗan bayan da mala’ikan ya yi magana da Maryamu, sai ta ziyarci Alisabatu. Da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu sai ɗan cikin Alisabatu ya motsa da ƙarfi a ciki. Matan sun yi murna tare domin abin da Allah ya yi masu. Bayan da Maryamu ta yi ziyarar wata uku gidan Alisabatu, sai ta koma gida.

Bayan da Alisabatu ta haifi ɗa namiji, Zakariya da Alisabatu suka raɗa masa suna Yahaya kamar yadda mala’ikan ya umurce su. Sai Allah ya ba Zakariya damar saka yin magana kuma. Zakariya ya ce, “Yabo ga Allah domin ya tuna da mutanensa! Kai ɗana, za a kira ka annabin Allah Maɗaukaki, wanda zai faɗawa mutane ƙaƙa za su sami gafarar zunubensu!”

Sura mai zuwa